Ticker

6/recent/ticker-posts

Header Ads Widget

Responsive Advertisement

JAMB ta fitar da sakamakon jararbawar 2025

 

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu ta Najeriya JAMB ta fitar da sakamakon jarrabawar wannan shekarar da aka gudanar makonnin da suka gabata.

Rajistaran hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede ne ya bayyana haka a shalkwatar hukumar a lokacin ƙaddamar da fitar da sakamakon.

Sai dai hukumar ta ta riƙe sakamakon ɗalibai 39,834, waɗanda ta ce za ta yi bincike a kansu bisa zargin satar jarrabawam sannan kuma ana zargin kusan ɗalibai 80 da laifukan da suka shafi jarrabawa, inda jihar Anambra ke kan gaba.

Hukumar ta kuma bayyana cewa daga cikin ɗalibai 2,030,862 da suka yi rajistar jarrabawar, 71,705 ba su samu damar rubuta jarrabawar ba.

Post a Comment

0 Comments